INEC ta amince da sabbin jam'iyyu 14 tare da watsi da buƙatun ƙungiyoyi 157

INEC ta amince da sabbin jam'iyyu 14 tare da watsi da buƙatun ƙungiyoyi 157




 Hukumar zaɓen Najeriya INEC ta amince da sabbin jam'iyyun siyasa 14 a ƙasar, da za su shiga harkokin zaɓukan ƙasar.


Cikin wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na X, ta ce ƙungiyoyi 171 ne suka gabatar mata da buƙatunsu na yi musu rajista domin zama jam'iyyu a ƙasar.


INEC ta ce bayan nazari tare da ɗora buƙatun ƙungiyoyin a ma'aunin sashe na 222 na kundin tsarin mulkin ƙasar da sashe na 79 (1,2 da 4) na dokar zaɓe ta 2022 kan ƙa'idar zama jam'iyya.


''Daga ƙarshe ƙungiyoyi 14 ne suka cika ƙa'idar hukumar zaɓen, yayin da sauran ƙungiyoyi 157 suka gaza cika ƙa'idar'', in ji hukumar ta INEC.


Sabbin jam'iyyun da hukumar ta amince da su sun haɗa da:


ATP

ADA

ANC

ASP

AAP

CDA

DLA

GRIP

GFP

LPP

NDP

NRP

PPA

PFP

Comments